Sojojin Somaliya Sun Kai Farmaki Kan Maboyar 'Yan Ta'addan Kungiyar Al-Shabab
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i24599-sojojin_somaliya_sun_kai_farmaki_kan_maboyar_'yan_ta'addan_kungiyar_al_shabab
Sojojin gwamnatin Somaliya sun kai farmaki kan maboyar 'yan kungiyar Al-Shabab da ke shiyar kudancin kasar, inda suka yi nasarar halaka 'yan ta'adda tara.
(last modified 2018-08-22T11:30:47+00:00 )
Oct 03, 2017 18:58 UTC
  • Sojojin Somaliya Sun Kai Farmaki Kan Maboyar 'Yan Ta'addan Kungiyar Al-Shabab

Sojojin gwamnatin Somaliya sun kai farmaki kan maboyar 'yan kungiyar Al-Shabab da ke shiyar kudancin kasar, inda suka yi nasarar halaka 'yan ta'adda tara.

Majiyar rundunar sojin Somaliya a yau Talata ta sanar da cewa: Sojojin kasar sun kai farmaki kan maboyar 'yan kungiyar Al-Shabab da ke yankin Gedo a shiyar kudancin kasar, inda suka yi nasarar kashe 'yan ta'adda tara tare da kwasar ganimar makamai masu yawa.

Hari kan maboyar 'yan ta'addan na kungiyar Al-Shabab a yankin Gedo ya zo ne kwana guda da 'yan ta'addan na Al-shabab suka kaddamar da wasu jerin hare-haren wuce gona da iri kan garuruwan kasar Somaliya da suke kusa da kan iyaka da kasar Kenya.