Nijeriya : An Gano Gawarwaki 16 Bayan Kifewar Kwale-kwale A Kebbi
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i24657-nijeriya_an_gano_gawarwaki_16_bayan_kifewar_kwale_kwale_a_kebbi
A Nijeriya ana ci gaba da neman wasu gawawakin mutanen da hatsarin kwale kwale ya rusa da su a jihar Kebbi dake arewacin kasar.
(last modified 2018-08-22T07:00:47+00:00 )
Oct 05, 2017 06:55 UTC
  • Nijeriya : An Gano Gawarwaki 16 Bayan Kifewar Kwale-kwale A Kebbi

A Nijeriya ana ci gaba da neman wasu gawawakin mutanen da hatsarin kwale kwale ya rusa da su a jihar Kebbi dake arewacin kasar.

Kawo yanzu dai an tsinto gawawarki 16 daga cikin mutum sama da 60 da kwale-kwale ya nitse da su a ranar talatan da ta gabata a garin Yawuri na jihar ta Kebbi.

Ana dai fargabar adadin wadanda suka mutu sanadin kifewar kwale kwalen ya karu, a yayin da akayi nasara ceto wasu uku da rai.

Bayanai sun nuna cewa kwale-kwalen ya bamki wani icce ne lamarin da ya sanya ya kife a tsakiyar kogin kwara.

Alkalumman da masu aikin ceto suka fitar sun nuna cewa sama da mutum 100 ne suka gamu da ajalinsu a irin wannan hatsarin a cikin wattani uku da suka gabata.