Mutane 33 Ne Suka Rasa Rayukansu Sanadiyyar Annobar Cutar Sankarau A Madagaska
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i24713-mutane_33_ne_suka_rasa_rayukansu_sanadiyyar_annobar_cutar_sankarau_a_madagaska
Gwamnatin kasar Madagaska ta bayyana cewa ya zuwa yanzu mutane 33 ne suka mutu daga cikin watan Augustan wannan shekara sanadiyyar annoban cutar sankarau a kasar
(last modified 2018-08-22T07:00:48+00:00 )
Oct 07, 2017 03:14 UTC
  • Mutane 33 Ne Suka Rasa Rayukansu Sanadiyyar Annobar Cutar Sankarau A Madagaska

Gwamnatin kasar Madagaska ta bayyana cewa ya zuwa yanzu mutane 33 ne suka mutu daga cikin watan Augustan wannan shekara sanadiyyar annoban cutar sankarau a kasar

Tashar talabijin ta France24 ta kasar Faransa ta nakalto jami'an gwamnatin kasar suna fadar haka a jiya Jumma'a, sun kuma kara da cewa mutane 200 suka kamu da cutar tun lokacin.

Baya ga haka labarin ya kara da cewa a matakan hana yaduwar wannan cutar gwamnatin kasar ta bada umurnin rufe jami'ar Antananarivo don feshin maganin hana yaduwar cutar, sannan ta samar da wurare na kiwon lafiya masu yawa a wurare daban-daban a duk fadin kasar.

Annobar Cutar Sankarau dai tana daga cikin cututtuka masu yaduwa tsakanin mutane kuma tana kama mutane da dabbobi.