Tsoffin Yan Sandan Biafra Sun Yi Maraba Da Biyansu Kudaden Ritaya
Tsoffin 'yan sandan Biafra a gabancin tarayyar Nigeria sun yi maraba da biyansu kudaden fansho bayan shekaru 47 da kawo karshen yakin basasa a yankin.
Kamfanin dillancin labaran Nigeria NAN ya bayyana cewa tsoffin yansandan Biafara wadanda aka yi masu afuwa a shekara ta 2000 sannan shugaban Buhari ya amince a biyasu kudaden ritayarsu sun yi murna da wannan matakin .
Babban sakatarin hukumar pensho Mrs Sharon Ikeazor ta fadawa tsoffin yansanda wadanda suka halarci taron bude shirin biyansu kudaden ritayansu a ranar Jumma'a kan cewa shugaban Buhari zai kawo karshen duk wahalhalun da suke ciki.
A hiran da NAN ta yi da wasu tsoffin yansandan Biafara sun nuna jin dadinsu da wannan matakin, sun kuma godewa shugaban kasar da tausayin da ya yi masu.
A makonnnin da suka gabata be shugaban Buhari ya amince a biya tsoffin yansandan biafara kudaden Penshon bayan da gwamnatin Obasanjo ta yi masu afwa a shekeata ta 2000.