Buhari Ya Damu Da Yadda Harkokin Ilmi Suke Tafiya A Tarayyar Nigeria
Shugaban tarayyar Nigeria Muhammadu Buhari ya bayyana matukar damuwarsa kan irin halinda bangaren ilmi da tarbiyya ta shi a kasar.
Jaridar Daily Trust ta Nigeria ta nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Litinin a wata zama na musamman da aka gudanar tare da jami'an gwamnatin da abin ya shafa a fadar shugaban kasar.
Shugaban ya kara da cewa yin watsi da harkokin ilmi wanda gwamnatocin da suka gabata suka yi ya kai ga a halin yanzu yara kimani miliyon 13.2 basa zuwa makaranta. Yawan jahilci ya kara yawa a kasar, makarantu sun lalace har ya kai ga babu kwararrun malaman da zasu karantar a makarantun kasar.
Buhari ya ce ci gaban ko wace kasa a duniya yana tafiya ne da yawan ilminta, don haka dole ne gwamnati ta yi wani shiri don sauya halin da bangaren ilmi yake ciki a kasar.
Kafin jawabinsa Ministan ilmi Malam Adamu Adamu ya bayyana cewa gwamnatin Buhari tana bukatar naira trillion guda a kowace shekara har na tsawon shekaru kafin ta cika alkawulan da ta yiwa mutanen Nigeria a bangaren ilmi.