Sojojin Kasar Kenya Sun Halaka Wasu Mayakan Kungiyar Al-Shabab Ta Somaliya
Sojojin gwamnatin Kenya da suke aiki karkashin rundunar wanzar da zaman lafiya ta kungiyar tarayyar Afrika a kasar Somaliya sun kashe wasu gungun 'yan ta'addan kungiyar Al-Shabab a yankin kudancin kasar ta Somaliya.
Kakakin rundunar sojin Kenya a cikin daren jiya Laraba ya fitar da sanarwar cewa: Sojojin gwamnatin Kenya da suke aiki karkashin dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika na "AMISON" a kasar Somaliya sun yi wani dauki ba dadi da mayakan kungiyar ta'addanci ta Al-Shabab da suka yi kokarin kutsawa cikin sansanin dakarun kungiyar tarayyar Afrika a yankin yankin kudancin Somaliya, inda gumurzun ya yi sanadiyyar halakar 'yan ta'adda akalla goma sha tara.
Kakakin rundunar sojin ta Kenya ya kara da cewa; Sojojin Kenya sun yi nasarar kwasar ganimar tarin makamai da 'yan ta'addan suka zo da su da nufin yin amfani da su a kan dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar ta tarayyar Afrika.