Ana Fama Da Matasalar Karancin Man Fetur A Najeriya
Duk tare da umurnin gwamnatin tarayyar Nigeria ga ministan man fetur na kasar a ranar Laraba na ya gaggauta kawo karshen karancin man fetur a kasar hakan bai tabbata ba har jiya Litinin.
Jaridar Premiumtimes ta Nigeria ta bayyana cewa a binciken da ta gudanar a jiya litinin ta gano cewa har yanzun akwai layukan ababen hawa a mafi yawan gidajen mai a birnin Abuja da sauran birnen kasar.
A ranar Laraba da ta gabata ce ministan watsa labarai Lai mohammad ya fadawa yan jarida, bayan taron majalisar ministocin kasar kan cewa za'a kawo karshen karancin man fetur a fadir kasar a cikin karshen mako mai zuwa.
Har'ila yau kamfanin man fetur na kasar NNPC, ta bakin kakakin kamfanin Ndu Ughamadu, ya fadawa yan jaridu a ranar Laraba kan cewa zasu kawo karshen layukan ababen hawa a gidajen man fitu a Abuja da sauran biranen kasar cikin sa'o'i.
Premiumtimes ta tabbatar da cewa har ya zuwa jiya Litinin karancin mai sai dada karuwa yake sannan masu saida man a jarka-jarka sun sake bayyana a kan titunan biranen kasar.