Mayakan Boko Haram 1050 Sun Mika Kansu Ga Sojojin Nijeriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27071-mayakan_boko_haram_1050_sun_mika_kansu_ga_sojojin_nijeriya
Majiyar sojojin Najeriya a yau Asabar ta bayyana cewa mayakan boko haram 1050 ne suka yi mika kansu ga sojojin kasar sannan wasu da sama sun ranta na kare a cikin yankin tapkin chadi da kuma garin Monguno a jihar Borno Borno.
(last modified 2018-08-22T07:01:15+00:00 )
Jan 06, 2018 15:35 UTC
  • Mayakan Boko Haram 1050 Sun Mika Kansu Ga Sojojin Nijeriya

Majiyar sojojin Najeriya a yau Asabar ta bayyana cewa mayakan boko haram 1050 ne suka yi mika kansu ga sojojin kasar sannan wasu da sama sun ranta na kare a cikin yankin tapkin chadi da kuma garin Monguno a jihar Borno Borno.

Jaridar Daily Trust ta Nijerya ta nakalto Kanar Onyema Nwachukwu mataimakin daraktan shirin  Operation Lafiya Dole ta samar da zaman lafiya a yankin yana fadar haka a yau a birnin Maiduguri. 

Nwachukwu ya ce mayakan boko haram 250 daga reshen Al-Barnawi ne suka mika kansu ga sojojin Nijerya bayan barin wutan da aka yi masu a yankin tabkin Chadi. Sannan ya kara da cewa wasu mayakan 700 sun mika kansu ne ga sojojin Nijeria a garin Monguno.

Banda haka Nwachukwu ya ce wani babban komandan mayakan na boko haran Mamman Nura ya ji mummunan rauni sannan an kashe daya daga cikin matansa a wani harin da sojojin suka kai masu. Daga karshe ya ce wasu daga cikin wadanda suka arce sun mika kansu ga sojojin jumhuriyar Niger a yayinsa wasu kuma suna kokarin sajewa a cikin mutane a Kano, Gaidam, Hadeja, Gashuwa  da kuma arewacin jihar Jagawa. Don haka  ya bukaci mutanen wadannan yankuna su kula da sabbin fuskoki da suke shiga cikinsu.