Wasu Gwamnonin Arewacin Najeriya Sun Bukaci Shugaba Buhari Ya Yi Ta Zarce
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27263-wasu_gwamnonin_arewacin_najeriya_sun_bukaci_shugaba_buhari_ya_yi_ta_zarce
Wasu Daga Cikin Gwamnonin arewacin Najeriya sun bukaci Shugaba Muhammadu Buhari ya sake tsayawa takara a zaben 2019.
(last modified 2018-08-22T07:01:17+00:00 )
Jan 14, 2018 02:57 UTC
  • Wasu Gwamnonin Arewacin Najeriya Sun Bukaci Shugaba Buhari Ya Yi Ta Zarce

Wasu Daga Cikin Gwamnonin arewacin Najeriya sun bukaci Shugaba Muhammadu Buhari ya sake tsayawa takara a zaben 2019.

Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya habarta cewa ya nakalto wasu gwamnonin bakwai na Jam'iyyar APC , na cewa  mafi dacewa shi ne shugaba Buhari mai shekaru 75 da haifuwa , ya zarce zuwa zagaye na biyu don ci gaba da gyara kasar.

A yayin ganawarsu da shugaban kasar Muhammadu Buhari bayan idar da sallar Juma'a a fadarsa ta Villa da ke birnin Abuja, dukkanin gwamnonin sun nuna goyon bayansu   da  kuma tabbatar da cewa za su yi dukkanin abin da ya dace na ganin shugaba Buhari ya zarce a zaben 2019.

Gwamnonin da suka nuna sha'awarsu na goyon bayan Shugaba Buhari, sun hada da na  jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje da na Kaduna Nasir El-rufa'i da Yahaya Bello na Kogi da Simon Lalong na Plateau da kuma Jubrilla Bindow na Adamawa da Ibrahim Geidam Yobe da Abubakar Bello na Niger, sannan kuma sun yi  wata ganawar sirri ta musamman da shugaban inda bakinsu ya hadu kan damarar da za su daura domin  tunkarar zaben na 2019.