Yan Bindiga Sun Sace Ba'amurke Guda Da Kuma Dan Canada A Nigeria
Yan bindiga sun sace wani ba Amurke da kuma dan kasar Canada guda a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a tarayyar Nigeria
Shafin yanar gizo na Sahara reporters ya bayyana cewa satar ta auku ne a ranar talatan da ta gabata. Labarin ya kuma kara kara da cewa yan bindigan sun kashe yansanda biyu da suke rakiyar turawan a lokacin satar.
Satar yan kasashen waje da kuma yan siyasa ya zama ruwan dare a tarayyar Nigeri a cikin watannin da suka gabata a duk fadin kasar . Yan bindigan sun maida aikin satar mutane don karban kudaden fansa a matsayin sana'a.
A wannan satar dai haryanzun ba'a ji doriyar mutanen ba, kuma babu wanda ya san abinda masu satar suke nema. Satar yan kasashen waje da kuma kashesu a wasu lokata a tarayyar ta Nigeria ya fi yawaita a yankin niger dalter saboda yawan ma'aikatan kamfanonin hakar man fetur a yankin. Barayin sukan nemi diyya na kudaden fansa masu yawa kafin su sake wadanda suka kaman.