AU Za Ta Kaddamar Da Shekara Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27533-au_za_ta_kaddamar_da_shekara_yaki_da_cin_hanci_da_rashawa
Kungiyar tarayya Afrika ta AU za ta kaddamar a hukumance da shekara nahiyar ta yaki da cin hanci da rashawa.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Jan 23, 2018 07:48 UTC
  • AU Za Ta Kaddamar Da Shekara Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Kungiyar tarayya Afrika ta AU za ta kaddamar a hukumance da shekara nahiyar ta yaki da cin hanci da rashawa.

An kaddamar da shirin ne a yayin taron kungiyar karo na 30 da aka fara a ranakun 22 zuwa 29 na watan nan a Birnin Adis Ababa na kasar Habasha.

Shugaban hukumar zartarwar ta kungiyar tne Musa Faki Mahamat ya sanar da hakan a yayin bude zaman taron wakilan din-din-din na kungiyar PRC) karo na 35 a kasar Habasha.

A cewar shugaban, taken taron kolin kungiyar na wannan karo, shi ne, "yaki da cin hanci da rashawa: hanya mai dorewa ta farfado da nahiyar Afirka".