Sudan Ta Ki Amincewa Da Shawarar Masar Akan Madatsar Ruwan Habasha
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27783-sudan_ta_ki_amincewa_da_shawarar_masar_akan_madatsar_ruwan_habasha
Ministan makamashi na kasar Sudan Mu'utaz Musa ne ya bayyana watsin da kasarsa ta yi da shawarar kasar Masar, tare da cewa nan da wani lokaci za a sake bude tattaunawa kan lamarin
(last modified 2018-08-22T07:01:21+00:00 )
Jan 30, 2018 15:31 UTC
  • Sudan Ta Ki Amincewa Da Shawarar Masar Akan Madatsar Ruwan Habasha

Ministan makamashi na kasar Sudan Mu'utaz Musa ne ya bayyana watsin da kasarsa ta yi da shawarar kasar Masar, tare da cewa nan da wani lokaci za a sake bude tattaunawa kan lamarin

Mu'utaz ya kara da cewa kasar tasa ba ta yarda da a mayar da batun madatsar ruwan ta zama ta kasa da kasa ba ko kuma a shigar da Bankin duniya  acikin lamarin.

A jiya litinin shugabannin kasashen Masar, Sudan da piraminstan Habasha suka yi ganawar  bayan fage a birnin Adis Ababa inda suka tattauna batun madatsar ruwan.

Sudan tana goyon bayan gina madatsar ruwan da Habasha take yi, saboda zai amfane ta ta fuskar noman rani da kuma samun wutar lantarki. Sai dai Masar na daukar madatsar a matsayin barazana a gare ta saboda yiyuwar raguwar kwararar ruwan Maliya zuwa cikin kasar.