Somaliya: An Sami Karin Wadanda Suka Rasu Sanadiyyar Tashin Bom
Feb 24, 2018 03:08 UTC
Rahotanni daga babban birnin kasar ta Somaliya sun ce adadin wadanda suka rasun ya karu zuwa 18 da kuma wasu 20 da suka jikkata
A jiya juma'a ne dai aka kai tagwayen hare-haren da motocin da aka makare da bama-bamai. Da fari jami'an tsaron kasar sun sanar da mutuwar mutane 3.
Kungiyar 'yan ta'adda ta Al-shabab ta dauki alhakin kai hari,
Shekaru masu tsawo kenan da kasar ta Somaliya take fama da tabarbarewar harkokin tsaro saboda rashin gwamnati mai karfi.
Kungiyar al-shabab tana a matsayin babban kalubalen tsaro ga gwamnatin Somaliya da kuma ta kasashen makwabta.
Tags