Somaliya : Yawan Mamata Bayan Harin Mogadishu, Ya Kai 32
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i28557-somaliya_yawan_mamata_bayan_harin_mogadishu_ya_kai_32
Hukumomin tsaron a Somaliya sun ce, yawan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon harin Mogadishu, babban birnin kasar ya karu zuwa 32.
(last modified 2018-08-22T07:01:28+00:00 )
Feb 25, 2018 07:21 UTC
  • Somaliya : Yawan Mamata Bayan Harin Mogadishu, Ya Kai 32

Hukumomin tsaron a Somaliya sun ce, yawan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon harin Mogadishu, babban birnin kasar ya karu zuwa 32.

Jerin hare haren na ranar Juma'a data gabata, an dai kai na farko ne da wata motar wani waje dake dab da hedkwatar hukumar lekan asiri da tsaro ta kasar Somaliya.

Bayan hakan kuma minti 15, an tayar da wani bom da aka ajiye a wata mota dake kan hanyar zuwa fadar shugaba.

Daga cikin wandanda hare haren suka rusa dasu a cewar hukumomin tsaron kasar, akwai dakaru 5, da kuma wani jami'in tsaro.

Kungiyar Al-Shabaab a Somaliyar ta ce ita ke da alhakin kai jerin hare haren.