Fara Aiwatar Da Shirin Musayar Fursunoni Tsakanin Kasashen Zambiya Da Namibiya
Mar 27, 2016 04:53 UTC
An fara shirin aiwatar da Yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kasashen Zambiya da Namibiya kan musayar fursunoni.
Shugaban hukumar kula da gidajen kurkuku a kasar Namibiya Raphael Tuhafeni Hamunyela ya bayyana cewa: Tun a shekara ta 2012 aka rattaba hannu kan yarjejeniyar musayar fursunoni tsakanin gwamnatocin kasashen Zambiya da Namibiya amma sai a wannan lokaci yarjejeniyar zata fara aiki.
Hamunyela ya kara da cewa: A halin yanzu haka kasarsa ta Namibiya tana da fursunoni biyu ne kacal a gidan kurkukun Zambiya, yayin da 'yan kasar ta Zambiya yawansu ya kai 89 a gidajen kurkukun Namibiya.
Tags