Alaka Tsakanin Kasashen Habasha Da Saudiyya Tana Ci Gaba Da Yin Tsami
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i31064-alaka_tsakanin_kasashen_habasha_da_saudiyya_tana_ci_gaba_da_yin_tsami
Bayan gwamnatin Habasha ta janye jakadanta daga Saudiyya, a halin yanzu kuma ta kirayi karamin jakadanta a kasar.
(last modified 2018-08-22T07:01:52+00:00 )
May 24, 2018 01:57 UTC
  • Alaka Tsakanin Kasashen Habasha Da Saudiyya Tana Ci Gaba Da Yin Tsami

Bayan gwamnatin Habasha ta janye jakadanta daga Saudiyya, a halin yanzu kuma ta kirayi karamin jakadanta a kasar.

Rahotonni sun bayyana cewa: Gwamnatin Habasha ta dauki wannan mataki ne a matsayin maida martani kan jinkirin da mahukuntan Saudiyya suka yi wajen sakin hamshakin attajirin nan dan asalin Habasha mazaunin kasar Saudiyya Muhammad Husaini Al-Amudi.

A makon da ya gabata fira ministan kasar Habasha Abiy Ahmed Ali ya kai ziyarar aikin kwanaki biyu a kasar Saudiyya, inda bayan dawowarsa ya yi furuci da cewa mahukuntan Saudiyya zasu saki Muhammad Husaini Al-Amudi, amma har yanzu babu labarin sakin nashi.

Tun a watan Nuwamban shekarar da ta gabata ce mahukuntan Saudiyya suke tsare da Muhammad Husaini Al-Amudi kan zargin barnata dukiyar kasa kasancewarsa cikin jerin hamshakan masu kudin kasar ta Saudiyya da Yarima mai jiran gado Muhammad bin Salma ya taso gaba.