Najeriya : MDD Ta Taimaka Wa Adamawa Don Yakar Cutar Kwalera
May 27, 2018 06:13 UTC
Majalisar Dinkin Duniya, ta taimaka wa yankin adamawa dake Najeriya da Dalar Amurka Miliyan biyu don murkushe cutar amai da gudawa ko Kwalera data bulla a yankin.
kawo yanzu dai mutane a kalla 50 ne cutar ta yi ajalinsu a arewa maso yammacin kasar ta Najeriya tun bayan barkewarta a kashen watan Maris da ya gabata.
Hukumar hana yaduwar annoba a Najeriya ta ce kimanin mutane dubu uku ne suka kamu da cutar ta kwalera a fadin kasar.
Ofishin kula da harkokin jin kai na MDD, wato OCHA, ya ce yana da fargabar yaduwar cutar a sansanonin 'yan gudun hijira na MDD, a don haka yake bukatar daukin gaggawa domin shawo kan matsalar.
Tags