Habasha Da Somalia Sun Bukaci A Yaki Ta'addanci
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i31792-habasha_da_somalia_sun_bukaci_a_yaki_ta'addanci
Shugabannin kasashen Somaliya da Habasha sun bukaci hadin gwiwar kasa da kasa domin yakar ayyukan ta'addanci a doron duniya.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Jun 17, 2018 13:05 UTC
  • Habasha Da Somalia Sun Bukaci A Yaki Ta'addanci

Shugabannin kasashen Somaliya da Habasha sun bukaci hadin gwiwar kasa da kasa domin yakar ayyukan ta'addanci a doron duniya.

A wata sanarwar bayan taro ta hadin gwiwa da bangarorin biyu suka fitar a Mogadishu, firaiministan kasar Habasha, Abiy Ahmed da shugaban kasar Somalia Abdullahi Mohamed Farmaajo, sun bayyana cewa, zaman lafiya da kwanciyar hankali su ne ginshikan tabbatar da ci gaban dukkan kasashen, kuma dukkanninsu sun amince za su yi aiki tare domin yakar ayyukan ta'addanci, ciki har da tunkarar manyan kalubalolin tsaro dake addabar iyakokin kasashen nasu.

Mista Ahmed wanda ya isa birnin Mogadishu domin ziyarar aiki ta kwana yini guda ya yabawa kokarin gwamnatin Somalia wajen magance kalubalolin tsaro da sauran batutuwan da suka shafi ci gaban kasar Somalia da dora kasar kan turbar dawwamamman zaman lafiya da ci gaba.

Kasashen biyu sun kuma nuna gamsuwarsu game da rawar da tawagar wanzar da zaman lafiya ta kungiyar tarayyar Afrika a Somalia wato AMISOM ke yi, wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Somalia.