Najeriya: Yawan Mamata A Harin Borno ya Karu
Jun 19, 2018 08:31 UTC
Kamfanin dillancin labarun Faransa ya ambato majiyar tsaron Najeriya na cewa; Adadin wadanda su ka kwanta damar sanadiyyar harin da aka a garin Damboa ya kai 43.
A sanarwar farko an ce mutane 31 ne su ka kwanta dama yayin da wasu da dama su ka jikkata.
Harin da aka kai na kunar bakin wake ne wanda ake gangantawa kungiyar Boko Haram.
Tun a 2009 ne dai kungiyar ta Boko Haram take kai hare-haren ta'addanci a Najeriya da kasashen makwabta da su ka hada Nijar, Kamaru, da Chadi.
Kawo ya zuwa yanzu kungiyar ta kashe mutanen da su ka kai 20,000, sai kuma wasu miliyan biyu da 600,000 da su ka zama 'yan gudun hijira.
Tags