Majalisar Dinkin Duniya Ta Kara Wa'adin Zaman Dakarunta A Kasar DR Congo
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i3187-majalisar_dinkin_duniya_ta_kara_wa'adin_zaman_dakarunta_a_kasar_dr_congo
Majalisar Dinkin Duniya ta kara wa'adin zaman dakarunta da suke aikin wanzar da zaman lafiya da sulhu a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo na tsawon shekara guda.
(last modified 2018-08-22T06:58:03+00:00 )
Mar 31, 2016 00:22 UTC
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Kara Wa'adin Zaman Dakarunta A Kasar DR Congo

Majalisar Dinkin Duniya ta kara wa'adin zaman dakarunta da suke aikin wanzar da zaman lafiya da sulhu a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo na tsawon shekara guda.

A zaman da ta gudanar a jiya Laraba: Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakin kara wa'adin ci gaba da zaman dakarunta da suke aikin wanzar da zaman lafiya da sulhu a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo na tsawon shekara guda tare da jaddada yin kira ga mahukuntan kasar da su gudanar da zabuka cikin gaskiya da 'yanci a duk fadin kasar.

Yau tsawon shekaru 16 ke nan da jibge dakarun wanzar da zaman lafiya da sulhu a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo lamarin da wasu mahukuntan kasar ke ganin lokaci yayi da za a sakarwa jami'an tsaron Dimokaradiyyar Congo ragamar wanzar da zaman lafiya da sulhu a kasarsu musamman ganin a halin yanzu an shawo kan manyan matsalolin tsaro da kasar ke fuskanta.