Najeriya: Ana Ci Gaba Da Zanga-zangar Neman Sakin Sheikh Elzakzaky
A jiya Laraba ne Mambobin Harkar Musulunci Su ka yi Zanga-zanga a birnin Kaduna suna masu kiran da a saki jagoransu Sheikh Ibrahim Yakubu El-zakzaky
Kamfanin dillancin labarun Fars na iran ya amabato kafafen watsa labarun Najeriya na nuni da cewa jami'an tsaro sun yi amfani da karfi wajen dakile Zanga-zangar inda suka jikkata wasu da dama.
A cikin watannin bayan nan Jahar kaduna ta zama inda mambobin harkar musuluncin suke yin Zanga-zangar neman sakin Sheikh El-Zakzaky baya ga babban birnin tarayya Abuja.
Tun a cikin watan Disamba na 2015 ne aka kama Sheikh El-Zakzaky tare da mai dakinsa Zenat bayan mummunan harin da sojojin kasar su ka kai a gidansa.
Bugu da kari harin ya yi sanadin mutuwar daruruwan almajiran shehun malamin da kuma 'ya'yansa.