Shugabannin 'Yan Sanda Na Kasashen ECOWAS Na Taro Kan Yaki Da Ta'addanci
Shugabannin 'yan sanda da kuma na tsaro na kasashen mambobin kungiyar raya arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS/CEDEAO, sun fara wani taron na yini uku a birnin Abidjan na kasar Ivory Coast mai manufar karfafa hadin guiwa don yaki da ta'addanci.
Ministan cikin gida na Ivory Coast, Sidiki Diakita, ay bayyana a gun taron cewa, wannan haduwar babbar dama ce da za'a iya amfani da ita idan aka yi la'akari da yanayin da ake ciki yanzu ta fuskar tsaro a yankin.
Taron zai duba hanyoyin da kasashen mambobin kungiyar zasuyi hadin gwiwa ta fuskar aikin 'yan sanda da sha'anin shari'a ta yadda jama'ar yankin zasu samu 'yancin walwala.
Masana sha'anin tsaro a Afrika da dama na ganin cewa, yaki da ta'addanci shi ne a sahun gaba a cikin matakan dake bukatar hadin guiwa a tsakanin kasashen mambobin kungiyar ta yammacin Afrika, don dakile ayyukan ta'addanci.