Rikicin APC: Bolaji Da Oshomole Sun Yi Magana Kan Sabuwar APC
Shugaban jam'iyyar APC mai mulki a tarayyar Nigeria Adams Oshomole ya bukaci yayan jam'iyyar wadanda suka yi fushi da ita su yi hakuri don a shrye yake ya sauraresu.
Jaridar Primiumtimes ta Najeriya ta Nakalto Oshomole yana fadar haka bayan da wasu yan jam'iyyar suka bayyana bellewar su a jiya Larabawa daga babbar Jam'iyyar.
Har'ila yau kakakin jam'iyyar Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa a shirye suke su saurari korafe -korafen yayan sabuwar jam'iyyar mai suna R-APC wato jam'iyyar APC wacce aka yiwa koskorima .
A jiya larabane Buba galadima shugaban sabuwar Jam'iyyar ta R-APC ta kasa ya bada sanarwan cewa kafa sabuwar jam'iyyar ta R-APC.
Korafe korafen sabuwar jam'iyyar dai sun hada da Zaben Oshiomole a matsayin shugaban jam'iyyar da kuma wasu mukamai 17 ba tare da bin tsarin da ya dace a cikin jam'iyyar ba.