Najeriya : Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutum 44 A Katsina
Rahotanni daga Najeriya na cewa, mutane 44 ne suka rasa rayukansu kana wasu 20 na daban suka bata sakamakon ambaliyar ruwan sama da aka samu a kashen makon jiya a jihar Katsina dake arewa maso yammacin kasar.
Gwamnan jihar Aminu Belllo Masari, ya shaidawa manema labarai jiya cewa, sama da gidaje 500 ne suka lalace a yankin karamar hukumar Jibiya dake jihar.
Aminu Masari, ya ce gwamnati ta tsugunar da wadanda iftila'in ya shafa a wata makarantar firamare dake yankin.
A cewarsa, ya sanar da gwamnatin tarayyar kasar game da iftila'in, ya na mai jadadda cewa tuni hukumar bada agajin gaggawa ta kai manyan motoci 13 shake da kayakin jin kai da za a raba ga mutanen, da wannan iftila'in da ba a taba gani ba a jihar Katsina da ma wasu sassan kasar ya shafa.