An Samu Bashin Naira Biliyan 1.6 Domin Biyan Albashin Kananan Hukumomin Abuja
Apr 01, 2016 08:40 UTC
Ministan babban birnin tarayyar Najeriya Abuja ya bayar da bashin Naira biliyan 1.6 domin biyan albashin ma'aikatan kananan hukumomin Abuja.
Bayan kwashe kimanin watanni 8 a jere ma'aikatan kananan hukumomin Abuja ba su samu albashi ba, Ministan babban birnin tarayyar Najeriya Abuja ya bayar da bashin Naira biliyan 1.6 domin biyan albashin nasu na watanni biyu.
Tags