An Samu Kusantuwa Tsakanin Eritrea Da Somaliya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i32561-an_samu_kusantuwa_tsakanin_eritrea_da_somaliya
Shugaban kasar Somalia, Mohamed Farmajo, ya kammala wata ziyarar aiki ta kwanaki uku a makofciyar kasar Eritrea, wacce aka bayyana da mai matukar tarihi.
(last modified 2018-08-22T07:02:11+00:00 )
Jul 31, 2018 06:46 UTC
  • An Samu Kusantuwa Tsakanin Eritrea Da Somaliya

Shugaban kasar Somalia, Mohamed Farmajo, ya kammala wata ziyarar aiki ta kwanaki uku a makofciyar kasar Eritrea, wacce aka bayyana da mai matukar tarihi.

Kasashen biyu dai sun shafe kusan shekaru 15 basu da huldar dflomatsiyya.

Amma a yayin wannan ziyarar kasashen biyu sun kulla yarjejeniyar maido da huldar diflomatsiyya da musayar jakadu a tsakaninsu.

An dai sanya hannu kan wannan yarjejeniya ce tsakanin shugaban kasar Eritrea Issaias Afeworki, da kuma takwaransa na Somalia, Mohamed Abdullahi Mohamed.