Shugaban Kasar Zimbabwe Ya Bukaci Hadin Kan Mutanen Kasarsa
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i32625-shugaban_kasar_zimbabwe_ya_bukaci_hadin_kan_mutanen_kasarsa
Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, bayan ya sami nasara a zaben shugaban kasar da aka gudanar a yan kwanakin da suka gabata a bukaci mutanen kasar da magoya bayansa da kuma yan adawa su zo su hada kai da shi don kawo ci gaba a kasar.
(last modified 2018-08-22T07:02:12+00:00 )
Aug 04, 2018 07:21 UTC
  • Shugaban Kasar Zimbabwe Ya Bukaci Hadin Kan Mutanen Kasarsa

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, bayan ya sami nasara a zaben shugaban kasar da aka gudanar a yan kwanakin da suka gabata a bukaci mutanen kasar da magoya bayansa da kuma yan adawa su zo su hada kai da shi don kawo ci gaba a kasar.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya nakalto Emmerson Mnangagwa yana fadar haka ne a shafinsa na "Tweeter" a yau Asabar. 

A jiya jumma'a ne hukumar zaben kasar Zimbabwe ta bada sakamakon zaben shugaban kasa na kashe, inda shugaban kasa mai ci Emmerson Mnangagwa ya sami kashi 50.8% na yawan kuri'in da aka kada a yayinsa babbar abokin adawarsa Nelson Chamisa ya tashi da kashi 44% na yawan kuri'un da aka kada. 

Bayan sanarda sakamakon zaben ne yan adawa suka fito zanga zanga wanda ya kai ga mutuwar mutane akalla 6 bayan da yan sanda suka yi kokarin tarwatsa su.