Boko Haram : An Kashe Sojojin Najeriya 7
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33566-boko_haram_an_kashe_sojojin_najeriya_7
Kamfanin dillancin labarun Faransa ya ambato wata sanarwa ta sojojin Najeriya da take cewa an kashe 7 daga cikinsu akan iyakar kasar da jamhuriyar Nijar.
(last modified 2019-04-27T14:25:10+00:00 )
Oct 11, 2018 12:20 UTC
  • Boko Haram : An Kashe Sojojin Najeriya 7

Kamfanin dillancin labarun Faransa ya ambato wata sanarwa ta sojojin Najeriya da take cewa an kashe 7 daga cikinsu akan iyakar kasar da jamhuriyar Nijar.

Bayanin ya ci gaba da cewa an kashe sojojin ne bayan taho mu gama da aka yi a tsakaninsu da 'yan kungiyar Boko Haram a jahar Borno da ke arewa maso gabacin kasar.

Sai dai sojojin na Najeriya sun kashe 'yan kungiyar ta Boko Haram da dama a yayin gumurzun.

Kungiyar ta Boko haram wacce take da alaka da Isis tana a matsayin babbar barazanar tsaro ga kasashen da suke a bakin tafkin Chadi.

Daga 2010 zuwa yanzu kungiyar ta kashe fiye da mutane 20,000 a cikin kasar ta Najeriya da kasashen makwabta.