Sabuwar Majalisar Tarayyar Afirka Ta Yi Zamanta Na Farko A Birnin Kigali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33764-sabuwar_majalisar_tarayyar_afirka_ta_yi_zamanta_na_farko_a_birnin_kigali
Zaman Majlisar da aka yi a jiya Litinin ya sami halartar wakilai 275 daga kasashen Afirka 55.
(last modified 2018-10-23T18:58:33+00:00 )
Oct 23, 2018 18:58 UTC
  • Sabuwar Majalisar Tarayyar Afirka Ta Yi Zamanta Na Farko A Birnin Kigali

Zaman Majlisar da aka yi a jiya Litinin ya sami halartar wakilai 275 daga kasashen Afirka 55.

'Yan Majalisar sun tattauna batutuwa daban-daban da su ka shafi nahiyar Afirka da matsalolin da take fuskanta daga cikin hadda batun samar da muhimman cibiyoyi na gwmanati da kuma bunkasa harkokin demokradiyya.

Shugaban kasar Rwanda Paul Kagame ne ya gabatar da jawabin bude zaman Majalisar inda ya yi magana akan muhimmancin rawar da Majalisar take takawa. Bugu da kari Kagame ya yi magana akan yadda Majalisar za ta taimaka wajen yi wa kungiyar  tarayyar Afirka kwaskwarima.

Shekaru 14 kenan da aka kafa Majalisar tarayyar Afirkan wacce take da manufar warware matsalolin da nahiyar take fuskanta.