Sojojin Najeriya Sun Ci Gaba Da Kashe 'Yan Shi'a
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33846-sojojin_najeriya_sun_ci_gaba_da_kashe_'yan_shi'a
Sojojin gwamnatin Najeriya sun bude wuta akan mabiya mazhbar Shi'a da ke tattakin arba'in a kusa da birnin tarayya Abuja
(last modified 2018-10-30T12:18:45+00:00 )
Oct 30, 2018 12:18 UTC
  • Sojojin Najeriya Sun Ci Gaba Da Kashe 'Yan Shi'a

Sojojin gwamnatin Najeriya sun bude wuta akan mabiya mazhbar Shi'a da ke tattakin arba'in a kusa da birnin tarayya Abuja

Kamfanin dillancin labarun Reuters ya ambato cewa daruruwan 'yan shi'ar kasar sun gudananr da Zanga-zanga suna masu yin kira da a saki jagoransu na harka Islamiyya, sheikh Ibrahim Yakubu El-zakzaky.

A jiya an ambaci cewa adadin wadanda su ka kwanta dama sanadiyyar kisan da sojojin su ka yi musu a yankin Cujo ya kai 16,yayin da wasu masu yawa su ka jikkata.

Tun a ranar 13 ga watan Disamba na 2015 ne aka kame Shekih el-zakzaky tare da mai dakinsa malama Zinat, bayan kisan gillar da aka yi wa daruruwan mabiyansa a birnin Zaria.

A shekaran jiya Lahadi ma an sami wadanda su ka kwanta dama sanadiyyar bude musu wuta da sojoji su ka yi a yankin Zuba.