MDD Ta Yi Allawadai Da Kisan Mutane A Harin Boko Haram
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33889-mdd_ta_yi_allawadai_da_kisan_mutane_a_harin_boko_haram
Majalisar dinkin duniya ta yi allawadai da harin da mayakan boko haram suka kai kan sansanin yan gudun hijira a birnin Maiduguri na jihar Borno a tarayyar Najeriya.
(last modified 2018-11-02T13:22:01+00:00 )
Nov 02, 2018 13:22 UTC
  • MDD Ta Yi Allawadai Da Kisan Mutane A Harin Boko Haram

Majalisar dinkin duniya ta yi allawadai da harin da mayakan boko haram suka kai kan sansanin yan gudun hijira a birnin Maiduguri na jihar Borno a tarayyar Najeriya.

Jaridar Premiumtimes ta Najeriya ta nakalto jami'i mai kula da ofishin majalisar a Abuja Edward Kallon yana cewa harin ya auku ne a daren laraba da ya gabata, sannan wannan shi ne hari mafi muni a baya bayan nan, wanda mayakan boko haram suka kai kan fararen hula.

Labarin ya kara da cewa hare-haren sun yi sanadiyyar mutuwar mutane 8 da kuma kama wasu mata. Majalisar ta kara da cewa yan gudun hijira kimani 12,600 ne suke samun mafaka a sansanin tun bayan kauracewar yankunansu da suka yi a shekarun bayan, sanadiyyar hare-haren mayakan na boko haram. 

Jami'i mai kula da bangaren sadarwa na hukumar OCHA, ita ma ta majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa an kai harin ne a sansanin yan gudun hijira da ke kusa da kauyen Dalori kusa da birnin Maiduguri a dai-dai lokacin faduwar rana, don haka mayakan na boko haram sun sace kayakin abicni a cikin gidajen mutane da dama a kauyen.