Najeriya : Kungiyar ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki
Nov 05, 2018 11:14 UTC
Kungiyar malaman jami'a ta Najeriya, cewa da ASUU ta shiga wani yajin aikin sai baba-ta-gani daga yau Litini.
Yajin aikin dai ya biyo bayan taron da kwamitin zartarwa na kasa na kungiyar ta ASUU ya yi jiya Lahadi a jihar Ondo.
Kungiyar ta zargi gwamnatin Najeriya da gaza aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla a baya game da yadda za a inganta yanayin aiki a jami'o'in kasar.
Yawaitar yajin aiki daga malaman jami'o''in na tasiri kan sha'anin ilimi a wannan kasa ta Najeriya, mafi yawan al'umma a Nahiyar Afrika.
Tags