MDD Na Son A Dage Zaben Libiya Har Zuwa 2019
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34005-mdd_na_son_a_dage_zaben_libiya_har_zuwa_2019
Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci da a dage zabe a kasar Libiya har zuwa shekara 2019 mai zuwa.
(last modified 2018-11-09T06:38:14+00:00 )
Nov 09, 2018 06:38 UTC
  • MDD Na Son A Dage Zaben Libiya Har Zuwa 2019

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci da a dage zabe a kasar Libiya har zuwa shekara 2019 mai zuwa.

Wakilin MDD, a Libiya ya bayyana cewa za'ayi wani taron kasa a farkon shekara 2019, sannan a gudanar da zabe a kasar.

M. Ghassan Salame, ya bayyana wa kwamitin tsaro na MDD cewa taron zai baiwa 'yan Libiyar damar tattauna makomar kasarsu.

A watan Disamba mai zuwa na shekara 2018 din nan ne aka tsara za'a gudanar da zaben na Libiya.