Madagaska : Kotun Tsarin Mulki Ta Amince Da Sakamakon Zabe Zagaye Na farko
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34273-madagaska_kotun_tsarin_mulki_ta_amince_da_sakamakon_zabe_zagaye_na_farko
Kotun tsarin mulki a Madagaska, ta yi na'am da sakamakon zaben shugaban kasar zagaye na farko, da hukumar zaben kasar (CENI), ta sanar yau kusa da mako biyu.
(last modified 2018-11-29T05:39:43+00:00 )
Nov 29, 2018 05:39 UTC
  • Madagaska : Kotun Tsarin Mulki Ta Amince Da Sakamakon Zabe Zagaye Na farko

Kotun tsarin mulki a Madagaska, ta yi na'am da sakamakon zaben shugaban kasar zagaye na farko, da hukumar zaben kasar (CENI), ta sanar yau kusa da mako biyu.

Sakamakon zaben da hukumar ta CENI ta fitar da ya nuna dan takara Andry Rajoelina ne kan gaba da  39,23% a yayin da Marc Ravalomanana ya samu 35%.

Hakan ne ya bada damar zuwa zagaye na biyu a zaben shugaban kasar tsakanin 'yan takara Andry Rajoelina da Marc Ravalomanana. 

A ranar 19 ga watan Disamba mai shirin kamawa ne za'a gudanar da zaben shugaban kasar ta Madagaska a zagaye na biyu, a yayin da za'a fara yakin neman zaben a ranar 4 ga watan na Disamba.