Najeriya/Zaben 2019 : Atiku Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya
Dec 13, 2018 10:53 UTC
Dan takarar babbar Jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar, ya sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a yayin zaben kasar na 2019 dama bayansa.
Alhaji Atiku Abubakar ya sanar da hakan ne a shafinsa na Twitter, da yammacin jiya Laraba.
Tsohon mataimakin shugaban kasa a Najeriyar, kana babban abokin hammaya na shugaban kasar Muhammadu Buhari, bai halarci taron sanya hannu kan yarjejeniyar ba a yayin taron da aka shirya a ranar Talata data gabata ba.
Samar da kwanciyar hankali a yayin zabuka a shi ne kusan babban abunda ake bukata a wannan kasa ta Najeriya, inda rikice-rikice masu nasaba da kabilanci da addini ke haddasa zaman dar-dar a yayin zabuka.
Tags