An Shelanta Dokar Ta Baci A Sudan Saboda Karin Tashe-Tashen Hankula
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34503-an_shelanta_dokar_ta_baci_a_sudan_saboda_karin_tashe_tashen_hankula
Gwamnatin kasar Sudan ta shelanta doka ta baci a kasar a dai-dai lokacinda zanga-zanga ta masu korafi kan tsadar rayuwa wanda ya hada da na abinci da bukatun yau da kullum yake kara bazuwa a kasar.
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Dec 20, 2018 15:35 UTC
  • An Shelanta Dokar Ta Baci A Sudan Saboda Karin Tashe-Tashen Hankula

Gwamnatin kasar Sudan ta shelanta doka ta baci a kasar a dai-dai lokacinda zanga-zanga ta masu korafi kan tsadar rayuwa wanda ya hada da na abinci da bukatun yau da kullum yake kara bazuwa a kasar.

Shafin yanar gizo na Sudan ya bayyana cewa gwamnatin kasar Sudan ta dauki wannan matakin ne bayan da zanga-zanga ta tsadar rayuwa yake yaduwa a yankuna da dama na kasar.

Labarin ya kara da cewa a birnin Atbara da kuma Port Sudan inda shugaban kasar ta Sudan Umar Hassan El-Bashir yake halattar atisai na jiragen yaki, mutane zun fito zanga-zanga don nuna matsin da suke ciki saboda tsadar abinci da kayakin bukatun yau da kullum. 

Komitin tsaro na birnin Atbara ta shelanta doka hana fita daga 6 na safe zuwa 6 na yamma, sannan sun rufe dukkan makarantu a birnin sai abinda hali yayi.

A jiya Laraba masu zanga-zanga sun kona ofishin jam'iyya mai mulkin kasar a birnin Atraba, sun kuma buka ce gwamnati ta yi murabus.

A birnin Khartum babban birnin kasar ma, mazu zanga-zanga sun yi ta kota tsoffin tayoyi da kuma rare taken "ba yunwa ba tsada".

Wasu labarai sun bayyana cewa an fara samun karancin makamashi a wasu yankuna a kasar ta Sudan a cikin yan kwanakin da suka gabata.