Somaliya Ta Kori Wakilin Majalisar Dinkin Duniya
(last modified Wed, 02 Jan 2019 07:06:28 GMT )
Jan 02, 2019 07:06 UTC
  • Somaliya Ta Kori Wakilin Majalisar Dinkin Duniya

Ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Somaliya ta bayyana wakilin majalisar Dinkin Duniya a kasar, Nicholas Haysom da cewa mutum ne da ba a maraba da shi a kasar.

Ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Somaliya ta zargi wakilin na Majalisar Dinkin Duniya da tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar.

Shi dai Haysom ya bukaci gwamnatin Somalia da ta yi bayani akan kame Mukhtar Robow wanda tsohon dan kungiyar al-shabab ne amma ya sauya zuwa dan siyasa. Har ila yau wakilin na Majalisar Dinkin Duniya ya yi tir da kisan da aka yi wa magoya bayan Robow a lokacin da su ka gudanar da Zanga-zanga

Antonio Gutrress ne dai ya dana Nicholas Haysom a matsayin wakilin Majalisar Dinkin Duniya a Somaliya a cikin watan Disamba na shekarar 2018 da ta kare.