Najeriya: Sojoji Sun Dakile Wani Harin Boko Haram A Buni-Yadi
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34892-najeriya_sojoji_sun_dakile_wani_harin_boko_haram_a_buni_yadi
Runduna ta 27 ta sojojin Najeriya da kuma sojoji a makarantar sojoji ta Musamman a Buni-Yadi na jihar Yobe a tarayyar Nageriya sun bada sanarwar dakli wani harin mayakan Boko Haram a kan sansaninsu da ke garin.
(last modified 2019-01-21T11:57:18+00:00 )
Jan 21, 2019 11:57 UTC
  • Najeriya: Sojoji Sun Dakile Wani Harin Boko Haram A Buni-Yadi

Runduna ta 27 ta sojojin Najeriya da kuma sojoji a makarantar sojoji ta Musamman a Buni-Yadi na jihar Yobe a tarayyar Nageriya sun bada sanarwar dakli wani harin mayakan Boko Haram a kan sansaninsu da ke garin.

Manjo Nuraini Alimi darakta mai kula da hulda da jami'an na Rundunar ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN a jiya Lahadi kan cewa, mayakan boko haram sun kawo farmako kan makarantar sojoji ta musamman da ke Buni-yadi da misalin karfe 4:15 a jiya Lahadi, inda rundunar ta maida masu martani, ta kuma halaka da dama daga cikinsu, a yayinsa wasu suka tsira da raunuka a jikinsu. 

Manjo Nuraini ya kara da cewa sojojin rundunar 4 n4 suka sami yan raunuka a fafatawar , kuma a halin yanzu suna jinya. 

Daga karshe Nuraini ya tabbatar da cewa sojojin Rundunar suna cikin hali mai kyau don fuskantar makiya.