An Rantsar Da Alkalan Kotunan Zabe Mai Zuwa A Tarayyar Najeriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34975-an_rantsar_da_alkalan_kotunan_zabe_mai_zuwa_a_tarayyar_najeriya
Mukaddashin Alkalin Alkalai na Najeriya ya rantsar da alkalai da masu taimaka masu 250 na kotunan sauraron koke=koken zabubbuka masu zuwa .
(last modified 2019-01-27T19:08:42+00:00 )
Jan 27, 2019 19:08 UTC
  • An Rantsar Da Alkalan Kotunan Zabe Mai Zuwa A Tarayyar Najeriya

Mukaddashin Alkalin Alkalai na Najeriya ya rantsar da alkalai da masu taimaka masu 250 na kotunan sauraron koke=koken zabubbuka masu zuwa .

Kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ya bayyana cewa mukaddashin alkalin alkalan Najeriya mai shari'a Tanko Muhammad ya yi kira ga alkalai da masu taimakamasu 250 na kutunan sauraron koke-koke a zabubbuka mai zuwa a kasar da su ji tsaron Allah a ayyukansu. 

Mai shari'a Mohammad ya kara da cewa ma'aikatar shari'a a kasar tana cikin jarrabawa mai tsanani, don haka ya bukaci alkalan da mataimakansu su yi aikinsu tsakaninsu da Allah a koke-kuken da za'a gabatar masu a zaben na wannan shekara ta 2019.

Masu shari'a 15 ne suka halarcin bikin rantsar da alkalan da kuma mataimakansu a Abuja, sannan Mai shari'a Sidi Bage na daga cikin wadanda suka halarci bikin.

A jiya ne shugaban Mohammadu Buhari ya rantsar da Mai shari'a Tanko Muhammad a matsayin mukaddashin alkalin alkalan kasa, bayan da ya sauke wanda ya gada saboda matsalolin sahria da yake fuskanta.