Djibouti : 'Yan Adawa Sun Kalubalanci Zaben Omar Guelleh
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i3643-djibouti_'yan_adawa_sun_kalubalanci_zaben_omar_guelleh
'Yan adawa a Djibouti sun kalubanci zaben shugaban kasar da Ismail Omar Guelleh ya lashe da gagarimin rinjaye.
(last modified 2018-08-22T06:58:06+00:00 )
Apr 09, 2016 10:45 UTC
  • Mohamed Tourtour dan takara indifanda a Djibouti
    Mohamed Tourtour dan takara indifanda a Djibouti

'Yan adawa a Djibouti sun kalubanci zaben shugaban kasar da Ismail Omar Guelleh ya lashe da gagarimin rinjaye.

Shugaban kasar Ismail Omar Guelleh , wanda yake shugabancin kasar tun shekara ta 1999 ya sake lashe zaben kasar da aka gudanar jiya Juma’a, a karo na hudu jere da kashi 86.68% na yawan kuriu da aka jefa, kamar yadda hukumomin kasar suka sanar.

'yan adawa dai na cewa anyi arangizon kuri'u, sanan an hana dayewa daga cikin wakilan shiga runfunan zabe.

Dama kafin hakan wasu daga cikin jam'iyyun adawa sun kauracewa zaben.

Kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun zargi shugaban kasar da tauye 'yan cin jama'a.