Sudan Ta Koka Kan Matsalar Fataucin Kananan Yara A Yankin Gabashin Afrika
Ministan harkokin cikin gidan kasar Sudan ya koka kan yadda matsalar fataucin mutane musamman kananan yara ke ci gaba da habaka a yankin gabashin Afrika.
Shafin Al-Yaumus-Sabi'i ya watsa rahoton cewa; Ministan harkokin cikin gidan kasar Sudan Ismat Abdur-Rahman Zainul-Abideen ya koka kan matsalar habakar fataucin mutane musamman kananan yara tare da kokarin mai da kasarsa tamkar hanyar shiga da su cikin kasashen gabashin Afrika.
Zainul-Abideen ya kara da cewa; Gwamnatin Sudan tana da karfin da zata iya shawo kan matsalar fataucin mutanen tare da kawo karshensa domin a halin yanzu haka ma ta jibge jami'an tsaronta a kan dukkanin hanyoyin da ake amfani da su wajen safarar mutanen.
Har ila yau ministan harkokin cikin gidan kasar ta Sudan ya yi gargadi kan masifar da ta kunno kai a tsakanin daliban jami'ar kasar ta yin amfani da muggan kwayoyi musamman a tsakanin matasa.