Mu'assasar Rasulul A'azam Ta Gabatar Da Takarda A Kwamitin Binciken Rikicin Zaria
Apr 24, 2016 08:03 UTC
A yau Alhamis ne Cibiyar Rasulul A'azam (RAAF) da ke birnin Kano ta gabatar da takarda a gaban kwamitin da gwamnatin Jihar Kaduna ta kafa don binciko musabbabin rikicin da ya faru a Zaria, tsakanin sojoji da 'yan kungiyar Harkar Musulunci.
Babban sakataren kungiyar ta RAAF Sheikh Saleh Muhammad Sani Zariya ne ya gabatar da takardar a madadin shugaban kungiyar Sheikh Muhammad Nur Dass.
Bayan kammala gabatar da takardar, Muhammad Awwal Bauchi daga nan Tehran ya tuntube shi don jin manufar su ta gabatar da takardar da kuma abin da takardar ta su ta kumsa
Ga hirar ta su
Tags