Gwamnatin Kasar Ivory Coast Ta Jaddada Aniyarta Ta Fada Da Ta'addanci
Feb 07, 2016 14:28 UTC
Gwamnatin Ivory Coast ta yi kira ga sauran kasashen yankin yammacin Afrika kan daukan matakan karfafa yaki da ayyukan ta'addanci a yankin.
Ministan mai kula da harkokin alaka tsakanin kasashen Afrika a gwamnatin Ivory Coast Ali Coulibaly ya jaddada yin kira ga kasashen yankin yammacin Afrika da su kara matsa kaimi a fagen yaki da ta'addanci da nufin kawo karshen wannan masifa a yankin baki daya.
Coulibaly ya kara da cewa: Baya ga masifar ayyukan ta'addanci a nahiyar Afrika, akwai kuma matsalar 'yan gudun hijira musamman matasa da suke halaka a teku a kokarin da suke yi na shiga cikin kasashen nahiyar Turai lamarin da ya zame dole a nemo hanyar magance wannan matsala cikin hanzari.
Tags