Alkalluman fararren hula dake mutuwa ya karu a Najeriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i4480-alkalluman_fararren_hula_dake_mutuwa_ya_karu_a_najeriya
Kungiyar AOAV mai yin nazari na tashin hanakali ta ce alkallumar fararen hular da suka mutu sanadiyar harin kungiyar Boko Haram a Najeria ya karu a shekarar da ta gabata.
(last modified 2018-08-22T06:58:11+00:00 )
Apr 28, 2016 00:49 UTC
  • Alkalluman fararren hula dake mutuwa ya karu a Najeriya

Kungiyar AOAV mai yin nazari na tashin hanakali ta ce alkallumar fararen hular da suka mutu sanadiyar harin kungiyar Boko Haram a Najeria ya karu a shekarar da ta gabata.

Rahoton da kungiyar ta fitar a Najeriya na cewa an samu karuwar alkaluman fararren hula dake rasa rayukansu a shekarar 2015 a kasar, fiye da shekarun hudu da suka gabata.

Kungiyar mai suna AOAV, ta ce hakan ya biyo bayan hare-haren kunar bakin wake da mayakan Boko Haram ke kaiwa musamman a yankin arewa maso yammaci kasa.

AOAV ta ce yawan mamata da kuma wadanda ke samun rauninka ya karu da kashi 190 fiye da yadda al’amarin yake a shekarun baya, Kuma Kashi 76 cikin 100 na mamatan farraren hula ne.

Rahoton ya ce yadda kungiyar ta boko haram ke amfani da dasa bama-bamai a kasuwanni, tashar motoci , masallatai da kuma guraren taruwa Jama'a, da kuma yadda suke amfani da manyan makamai wajen kai hari shi ne ya yi sanadiyar karuwar alkalluman.