Nijar : Nuna Adawa Da Takurawa Kungiyoyin Fararen Hula
Nuna Adawa Da Takurawa Kungiyoyin Fararen Hula
Kungiyoyin Fararen Hula A Jamhuriyar Nijar Sun yi tir da yadda hukuma ta ke takurawa kungiyoyin su da hana su aiwatar da ayyukansu.
Radiyon Kasa da kasa na Faransa ya ce a yau alhamis ne kungiyoyin farar hular na jamhuriyar Nijar su ka fitar da wani bayani da a ciki su ka bayyana cewa; An take mu su hakkokinsu mafi karanci da su ka hada da yin zanga-zanga.
Bugu da kari bayanin ya kunshi yin kira ga al'ummar kasa ta Nijar da fito kwansu da kwarkwatarsu domin yin zanga-zanga a gobe bayan idar da sallar juma'a domin yin Allah wadai da yi wa demokradiyya karen tsaye.
A ranar lahadin da ta gabata ne dai mahukuntan kasar su ka hana gudanar da Zanga-zangar da wata kungiyar farar hula ta shirya.