Burkina Faso : An Soke Sammacin Kame Compaore Da Guillaume Soro
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i4516-burkina_faso_an_soke_sammacin_kame_compaore_da_guillaume_soro
Kotun karya shari'a a Burkina Fasa, ta soke sammacin kasa da kasa na kotun sojin kasar kan kame tsohon shugaban kasar Blaise Compaore da kuma kakakin majalisar dokokin kasar Ivory Coast Guillaume Soro.
(last modified 2018-08-22T06:58:12+00:00 )
Apr 28, 2016 23:37 UTC
  • Guillome Soro da Blaise Compaoure
    Guillome Soro da Blaise Compaoure

Kotun karya shari'a a Burkina Fasa, ta soke sammacin kasa da kasa na kotun sojin kasar kan kame tsohon shugaban kasar Blaise Compaore da kuma kakakin majalisar dokokin kasar Ivory Coast Guillaume Soro.

A cewar babban mai shiga da kara na kotun, Armand Ouédraogo an soke dukkannin sammacin ne saboda ba'a bi hanyoyin da suka da dace ba, wanda a cewar sa ko da yaushe idan aka gyara su za'a iya fitar da sammacin.

A ranar 4 ga watan Oktoba bara ne kotun sojin burkina faso ta fitar da sammacin kame Mr Compaore dake gudun hijira a kasar Ivory Coast tun bayan zanga-zangar al'ummar kasar data yi awan gaba da mulkin sa a ranar 31 gatan Oktoba 2014.

Ana dai zargin Mr Compaore da hannu a kisan da akayi wa tsohon shugaban kasar Thomas Sankara a yayin juyin mulkin 15 ga watan Oktoba 1987.

kazalika kotun sojin kasar na zargin Mr Guillaume Soro kakakin majalisar dokokin kasar Ivory Coast da hannu a yunkurin juyin mulkin da baiyi nasara ba kan gwamnatin rikon kwarya ta Burkina Faso a watan Satumba bara.