An Kame 'yan kungiyar al-shabab 4
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i6073-an_kame_'yan_kungiyar_al_shabab_4
Jami'an tsaron sun kame 'yan kungiyar al-shabab Kusa da Birnin Mogadishu.
(last modified 2018-08-22T11:28:22+00:00 )
Jun 01, 2016 07:59 UTC
  • An Kame 'yan kungiyar al-shabab 4

Jami'an tsaron sun kame 'yan kungiyar al-shabab Kusa da Birnin Mogadishu.

Kamfanin Dillancin Labarun Xinuha ya ambato kakakin ma'aikatar tsaron cikin gidan Somaliya Abdy Kumayl Mu'allim Shukry yana fadin cewa; An kame 'yan al-shabab din ne a cikin wata mota wcce su ka makare da bama-bamai.

Kumayl Shukri ya ci gaba da cewa; 'yan kungiyar ta al-shabab suna da shirin kai hari ne a cikin birnin Mogadishu.

A cikin watannin bayan nan dai sojojin kasar ta Somaliya tare da dakarun tabbatar da zaman lafiya na nahiyar Afirka sun tsananta kai hare-hare akan sansanonin 'yan kungiyar ta al-shabab, tare da samun galaba akansu.