An kashe 'Yan bokoharam Da Dama A Najeriya
Sojojin Najeriya Sun Kashe 'yan Bokoharam da dama a Najeriya.
Kamfanin Dillancin Labarun Faransa ya ambato majiyar sojojin kasar ta Najeriya na sanarwa a jiya asabar cewa; Sun kashe 'yan kungiyar bokoaram 19 a jahar Borno.
Sanarwar Sojan ta ci gaba da cewa sun sami bayanai ne akan inda 'yan kungiyar a bokoharam a wani sansani.
Daga cikin wadanda aka kashe a lokacin wannan harin kamar yadda majiyar sojoin kasar ta ce; Da kawai Amir Abubakar Gana daya daga cikin kwamandojin kungiyar ta Bokoharam.
Wata majiyar ta ce sojoji biyu ne su ka jikkata sanadiyyar harin.
Daga bullar bokoharam a Najeriya a 2009 zuwa yanzu, sun kashe fiye da mutane 10,000, yayin da wasu dubun dubata su ka zama 'yan gudun hijira.