Jaddada Sunan Sudan cikin Jerin Kasashe masu Tallafawa Ta'addanci
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i6355-jaddada_sunan_sudan_cikin_jerin_kasashe_masu_tallafawa_ta'addanci
Gwamnatin kasar Sudan ta bayyana damuwarta da ci gaba da sanya kasar cikin jerin kasashe masu tallafawa ayyukan ta'addanci a duniya na ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka.
(last modified 2018-08-22T06:58:24+00:00 )
Jun 07, 2016 02:26 UTC
  • Jaddada  Sunan Sudan cikin Jerin Kasashe masu Tallafawa Ta'addanci

Gwamnatin kasar Sudan ta bayyana damuwarta da ci gaba da sanya kasar cikin jerin kasashe masu tallafawa ayyukan ta'addanci a duniya na ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka.

Gwamnatin kasar Sudan ta bayyana damuwarta da ci gaba da sanya kasar cikin jerin kasashe masu tallafawa ayyukan ta'addanci a duniya na ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka.

Kamfanin dillancin labaran Chinhuwa na kasar China ya nakalto majiyar ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sudan tana bayyana haka a jiya Litinin ta kuma kara da cewa tare da duk hadin kai wanda gwamnatin kasar Sudan ta bayar bata ji dadin cewa har hanzu a kwai sunanta a cikin jerin sunayen cikin kasashen masu tallafawa ayyukan ta'addanci a kundin ma'aikatar harkokin wajen Amurka ba. Ma'aikatar da musanta dukkan tuhume tuumen da wasu hukumomi a kasar Amurka takewa gwamnatin kasar kan abinda ya shafi ayyukan ta'addanci a duniya.

Tun shekara ta 1993 gwamnatin kasar Amurka ta sanya Sudan a cikin jerin kasashe masu tallafawa ayyukan ta'addanci a duniya, sannan ta fara doramata dakunkumai a kan wannan lamari a shekara ta 1997.