Najeriya : Tsagerun Niger-delta Sun Yi Fatali Da Bukatar Tattaunawa
Jun 08, 2016 06:47 UTC
'Yan a ware na Niger-delta Avangers sun yi fatali da bukatar gwamnatin Nigeria ta tattaunawa.
A cikin wata sanarwa da tsagerun na NDA suka wallafa a shafinsu na Twitter, sun ce babu batun wata tattaunawa da duk wani kwamiti.
A ranar Litinin nan ce dai babban sakataren gwamnatin Nigeria na man fetur, Emmanuel Ibe Kachikwu ya sanar ga manema labarai cewa an dakatar da duk wani yunkuri soji a yankin na Niger- delta na akalla tsawan mako biyu domin baiwa kowa da kowa damar shiga tattaunawa.
Hare-haren da 'yan Niger delta ke kaiwa kan bututan man fetur sun dai harfar da kasar mumunan koma baya harkokin fitar da man fetur din da ta dogara dashi.
Tags